1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Nederlands ta yi murabus

June 30, 2006
FM NL Jan Peter Balkenende ya mika takardun yin murabus din gwamnatinsa a hukumance ga sarauniya Beatrix. Wannan mataki zai share fagen gudanar da sabon zabe na gaba da wa´adi, wanda ake sa rai za´a yi a karshen wannan shekara. A jiya alhamis ´ya´yan jam´iyar D66 wadda ita ce karama a cikin gwamnatin kawance sun ajiye mukamansu a majalisar ministoci bayan yunkurin da aka yi na karbe takardun zama ´yar kasar NL daga ´yar asalin Somalia kuma ´yar majalisa Ayaan Hirsi Ali ya ci-tura. Ministar kula da zaman baki a cikin kasar ta NL Rita Verdonk ta fara tayar da batun karbewa Hirsi Ali takardun zama ´yar kasar bayan da ´yar asalin Somaliar ta amsa cewar ta ba da bayanai na karya a lokacin da ta gabatar da takardun neman mafakar siyasa. To amma daga baya an mayar mata da takardun zama ´yar kasar.