1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Siriya ta fara yunkurin daidaita rikicin kasarta

November 3, 2011

A karon farko Siriya ta amince da yarjejeniyar da kungiyar hadin kan Larabawa ta gabatar mata na shiga tattaunawa da masu adawa

Wakilan kungiyar hadin kan LarabawaHoto: picture-alliance/dpa

Kungiyar hadin kan larabawa ta ce gwamnatin Siriya ta amince ta aiwatar da shirinta wanda zai kawo karshen watannin da aka shafe ana zud da jini a kasar. Frime Ministan Katar, Hamad Bin Jassim al Thani, shine ya bada wannan sanarwar lokacin wata hirar da ya yi da manema labarai a birnin Alkahira. Wannan shiri dai ya tanadi gwamnati a damaskus da ta janye dakarunta daga kan tituna, ta kuma sako fursunonin siyasa. Ya kuma hada da baiwa masu sanya ido a kungiyar larabawa da 'yan jarida 'yancin gudanar da ayyukan su a kasar ba tare da matsin lamba ba. To sai dai wasu jami'an diplomasiyya sun nuna shakkunsu suna masu cewa Shugaba Bashar AL-Assad ba zai yi amfani da wannan shiri ba.

Masu fafutukar kare hakkin bil adama sun ce a tsakanin sao'i 24 da suka wuce yanzu mutane 20 sun mutu.

Mawallafiya: Pinado Abdu

Edita          : Umaru Aliyu