Burkina Faso ta musanta halaka makiyaya da dama
March 16, 2025
Gwamnatin sojin Burkina Faso ta musanta zargin halaka fararen hula, matakin da ya haifar da takaddama da kiraye-kirayen tabbatar da adalci daga kungiyoyin kare hakkin 'dan Adam.
Karin bayani:Human Rights ta bukaci binciken kisan mutane a Burkina Faso
Gwamnatin gwamnatin mulkin sojin ta ce masu yada wadanda labarai ta kafafen sada zumunta na yin hakan ne domin haifar da rudani a kasar da ke cikin kwanciyar hankali.
Karin bayani: Sabon babi a yaki da ta'addanci a Sahel
Wasu hotunan bidiyo da suka karade shafukan sada zumunta sun nuna wasu gawarwaki na makiyaya maza da mata da har ma da kananan yara a daddaure. Kungiyar kare hakkin bil Adama ta HRW ta yi kira ga gwamnatin soja da ke mulki a Burkina Faso, da ta gudanar da cikakken bincike kan wannan mummunan kisan gilla da aka yi wa gomman fararen hula a yankin Solenzo na yammacin kasar.