1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin gwamnati za su afkawa Mekele

Zainab Mohammed Abubakar
November 22, 2020

Sojojin gwamnatin Habasha sun yi barazanar afkawa Mekele, babban birnin Tigray kuma cibiyar gwamnatin wannan yanki da gwamnati ke neman rusawa.

Tigray-Konflikt | Äthiopisches Militär
Hoto: Ethiopian News Agency/AP/picture alliance

Kakakin rundunar Habasha Dejene Tsegaye ya sanar da cewar, mataki na gaba da ke gabansu shi ne yi wa birnin Mekele kawanya da tankunan yaki. Inda ya gargadi mazauna birnin dubu 500, da su yi kokarin cire wa kansu kitse a wuta tun suna da lokacin haka.

Tun a farkon wannan wata ne dai framinista Abiy Ahmed da ya samu lambar yabo ta Nobel a kan zaman lafiya a bara, ya umurci kaddamar da yaki a kan mayakan fafutukar 'yancin Tigray da ake kira TPLF a takaice, bayan zarginsu da kai hari kan sansanonin sojin gwamnati guda biyu da ke yankin.