Halin da ake ciki a gaza
July 9, 2006Talla
UN
Sakatare general na mdd Kofi Annan ya bukaci bawa jamian agajin majalisar daman shiga cikin zirin Gaza da gaggawa ,domin agazawa mazauna yankin.Mr Annan yayi wannan kira a jiya,adangane da yanayi daya bayyana na tausayi ga alummar palasdinawa dake gazan.Ya bayyana cewa harin da dakarun Izraela suka kaiwa cibiyar samarda wutan lantarki a gaza,ya kawo matukar damuwa a asibitoci da masamaantun abinci da ruwan sha da,muhalli mai tsabta.Akan hakane Kofi Annan yayi kira ga gwamnatin Izraela data dauki matakai na gaggawa na sake gyaran ,naurorin da dakarunta suka lalata.