Kungiyar Hamas ta rusa gwamnatinta a Gaza
July 6, 2026
Sanarwar ta fito ne bayan wani taron manema labarai da kakakin gwamnatin Hamas, Ismail al-Thawabta, ya gudanar a Deir al-Balah. Inda ya bayyana cewa an yanke shawarar rushe kwamitin gwamnatin Gaza tare da nada wani mutum da kowa zai amince da shi domin kula da harkokin gwamnatin na wucin gadi har sai sabon kwamitin gudanar da mulkin Gaza ya karbi aikinsa gaba daya.
A cewar Hamas, ma'aikatan gwamnati da kwararrun jami'an gudanarwa za su ci gaba da aikinsu na yau da kullum domin tabbatar da cewa ayyukan gwamnati ba su tsaya ba, yayin da ake gudanar da sauyin mulkin. Sai dai kungiyar ba ta bayyana takamaiman ranar da za a kammala mika mulki ba.
Hamas ta karbi ragama da ikon zirin Gaza tun a shekarar 2007 bayan rikici da kungiyar Fatah, kuma tun daga lokacin take tafiyar da harkokin mulki a yankin. Sai dai yakin da ya dade tsakanin Hamas da Isra'ila ya haddasa mummunar barna a Gaza, lamarin da ya kara matsin lamba na neman sabon tsarin gudanarwa da zai saukaka sake gina yankin da kuma inganta rayuwar fararen hula.
Masu nazarin siyasa na ganin wannan mataki na Hamas na iya zama muhimmin ci gaba wajen aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma bai wa sabon kwamitin kwararrun Falasdinawa damar jagorantar ayyukan farfado da Gaza. Sai dai sun yi gargadin cewa har yanzu akwai man'yan batutuwa da ba a warware ba, musamman kan makomar makaman Hamas da tsaro da kuma yadda za a tabbatar da cikakken mika ikon gudanar da mulki.
A halin yanzu, ana ci gaba da tattaunawa tsakanin masu shiga tsakani da bangarorin rikicin, domin tabbatar da dorewar tsagaita bude wuta da kuma kammala shirye-shiryen kafa sabon tsarin gudanar da harkokin Gaza.