SiyasaAfirka
Hare-harbe sun halaka mutane 13 a Afirka ta Kudu
June 10, 2026
Talla
A wannan Laraba, harbe-harben 'yan bindiga dadi sun halaka mutane 12 cikin unguwar 'yan rabbana ka-wadatamu na birnin , daya daga cikin manyan biranen kasar Afirka ta Kudu.
Laifuka na ta'azzara
Akwai kimanin 'yan bindiga guda 10 lokacin da aka samu harbe-harben.
'Yan sanda suna ci gaba da binciken dalilan wannan harbe-harbe, inda kasar ta Afirka ta Kudu take ganin matsalolin masu amfani da makamai wajen kawo tashe-tashen hankula, musamman wadanda ake dangantawa da hakar ma'adanai a kasar.
Afirka ta Kudu ta kasance kasa mafi ingancin tattalin arziki na zamani tsakanin kasashen Afirka, amma tana fama da matsalolin aikata miyagun laifuka musamman tsakanin matasa masu zaman kashe wando.