1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Lamuran tsaron Burkina Faso sun sukurkuce

Suleiman Babayo
August 20, 2021

Ana fargaba kan yawan mutanen da hare-haren 'yan ta'adda ya halaka a kasar Burkina Faso sun hausa 100.

Symbolbild I Sicherheitskräfte Burkina Faso
Hoto: Ahmed Ouoba/AFP/Getty Images

Ana tsoron mutanen da suka mutu sun kai 100 a hare-hare tsageru masu nasaba da jihadi a kasar Burkina Faso da ke yankin yammacin Afirka. Hukumomin tsaron sun bayyana halaka 'yan ta'addan fiye da 80, kuma rikicin ya raba fiye da mutane 400 da gidajensu kusa da iyakar kasar ta Burkina Faso da Mali.

Hare-hare masu matsanancin ra'ayin Islama na ci gaba kassara kasar ta Burkina Faso wadda ke sahun gaba a kasashe 'yan rabbana ka wadata mu, lamarin da ya shafi galibin kasashen yankin Sahel.