1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Somaliya: Harin bam ya ritsa da sojoji

Abdourahamane Hassane
June 15, 2024

Wani bam da mayakan al Shebab suka dana, ya fashe a yayin da ayarin motocin sojojin Somaliya ke wucewa, inda ya kashe sojoji akalla shida, ciki har da wani Kanal, a kudancin kasar.

Hoto: AP Photo/picture alliance

Fashewarbam din ya faru ne a lokacin wani sintiri a kusa da garin Gofgaduud mai tazarar kilomita 30 daga garin Baidoa da ke a  kudu maso yammacin kasar. Sama da shekaru 16  kenan masu kishin Islama ke yakar gwamnatin Somaliya Ko da yake a shekarar  ta 2011 dakarun Tarayyar Afirka sun fatattakesu daga babban birnin kasar, amma har yanzu suna a yankunan karkara na  somaliyar.