1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-haren ´yan tawaye a Somaliya

Ibrahim SaniDecember 13, 2007

Mutane tara a birnin Magadishu na ƙasar Somaliya sun rasa rayukansu.Hakan nada nasaba ne da wani hari da ´yan tawaye su ka kaine a kasuwar Bakara. Kafin kai harin, sai da ´yan tawayen su ka yi taho mu gama da sojin ƙasar, dake samun tallafin sojin Habasha. Rikicin ´yan tawayen a yanzu haka ya yi sanadiyyar rayuka da daman gaske a ƙasar. Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil adama sun ce a shekarar nan, mutane kusan dubu shidda ne su ka rasa rayukansu. Ywaitar rikice-rikice a ƙasar ya haifar ´yan Somaliya ci gaba da yin hijira, don tsira da rayukan su izuwa maƙotan ƙasashe.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW