1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari a kan asibitin soji a Kabul

Zainab Mohammed Abubakar
November 2, 2021

Kusan mutane 20 ne suka rasa rayukansu daura wasu sama da 50 da suka jikkata a wasu hare hare da aka kai a asibitin sojoji mafi girma a birnin Kabul na kasar Afghanistan.

Afghanistan Kabul | Anschlag auf Vize-Präsident Amrullah Saleh
Hoto: Rahmat GulAP/picture alliance

Rahotanni na nuni da cewar wani dan kunar bakin wake ne ya tayar da abubuwan fashewa da ke jikinsa a kofar shiga katafaren asibitin Sardar Mohammed Daud Khan mai gadajen jinya 400 da ke tsakiyar Kabul, daga nan kuma sai wasu 'yan bindiga suka fara buda wuta a cikin asibitin, a cewar gwamnatin Taliban.

Kakakin ma'aikatar lafiya ya sanar da cewar, an samu gawarwakin mutane 19, a yayin da aka yi jigilar sama da mutum 50 zuwa asibiti.

Harin na wannanTalatar dai, shi ne na baya bayannan a Afghanistan din tun bayan da 'yan Taliban suka kwace mulkin wannan kasa da yaki ya daidaita.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW