1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bam ya kashe mutane a Libiya

Abdul-raheem Hassan
May 25, 2018

Jami'an tsaro sun tabbatar da harin da aka kai cikin mota a tsakiyar birnin Benghazi, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane akalla 7 yayin da wasu kusan 20 suka jikkata.

Libyen Straßenkämpfe zwischen Armee und Ansar al-Scharia Milizen in Benghasi
Hoto: picture alliance/abaca/M. Elshaiky

Hukumomin tsaro sun ce bam din ya tashi ne cikin wata mota kusa da babban Otal din Tibesti, inda musulmai ke gangamin bukukuwan murna a watan azumin Ramadana. Babu wata kungiya da ta dau alhakin harin, amma hukumomin Libiya na zargin 'yan ta'adda da aka ci karfinsu a yankin ne ke yunkurin maida martani. A baya dai sojoji sun sanar da nasarar kakkabe tungar kungiyoyin ta'adda da ke birnin na Benghazi, tare da ayyana karbe iko da birnin bayan shafe shekaru uku ana gwabza fada.