SiyasaGabas ta Tsakiya
Harin Isra'ila ta sama ya halaka mutane 13 a Lebanon
June 10, 2026
Talla
Wani harin sojojin sama na Isra'ila ya halaka mutane 13 a yankin kudancin Lebanon a wannan Laraba. Hukumomin tsaron Lebanon sun ce Isra'ila tana kara kaimi hare-hare kan mayakan kungiyar Hezbollah da ke samun goyon bayan kasar Iran.
Halin da ake ciki
Zuwa yanzu imanin mutane 3,700 suka halaka sakamakon hare-haren Isra'ila a Lebanon tun farko watan Maris lokacin da fada ya doce, inda ma'aikatar kula da lafiya ta Lebanon ta ce kimanin wasu mutane milyan 1.2 sun tsere daga gidajensu, domin tserewa daga wuraren da ake fama da tashe-tahsen hankula tsakanin bangarorin na Isra'ila da mayakan Hezbollah.