SiyasaGabas ta Tsakiya
Harin Isra'ila ya halaka mutane biyar a Lebanon
September 21, 2025
Talla
Kamfanin dillancin labarai na Lebanon ya rawaito cewa Isra'ila ta kai farmakin ne a kusa da Bint Jbeil da ke kudancin birnin Beirut. Isra'ila dai ta kaddamar da hare-hare kan Lebanon da sunan farautar mayakan Hezbollah, duk da yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kasashen biyu a watan Nuwambar 2024, domin kawo karshen tashin hankalin.
Karin bayani: Israila ta kai hari Beirut karon farko bayan tsagaita wuta
A sakon da ya wallafa a shafinsa na X, Firaministan Lebanon Nawaf Salam ya ce da gangan Isra'ila ta kai farmakin kan fararen hula. Isra'ila dai ta zafafa hare-haren da take kai wa Lebanon a wannan mako.