1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kunar bakin wake a Kamaru

Abdullahi Tanko Bala
November 28, 2018

Wata 'yar kunar bakin wake ta jikkata mutane akalla 29 a yankin arewa mai nisa a kasar Kamaru.

Kamerun Soldaten gegen Boko Haram
Hoto: Reinnier KAZE/AFP/Getty Images

Akalla mutane 29 suka jikkata yayin da wata 'yar kunar bakin wake ta tarwatsa kanta a garin Amchide dake yankin arewa mai nisa a iyakar Najeriya da Kamaru, yankin da ya yi fama da harin 'yan Boko Haram.


Rahotanni sun ce sojoji sun sami nasarar harbe 'yar kunar bakin wake ta biyu wadda ta yi kokarin tada nakiyar da take dauke da ita.


Wani jami'in tsaro a yankin da ya bukaci a sakaya sunansa yace an kai harin ne a ranar da ake cin kasuwa a garin a kuma lokacin da ake tsakiyar hada hadar kasuwanci.