1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin ta'addanci a Bakasin Kamaru

February 12, 2011

Mutune biyu sun rigamu gidan gaskiya a wani hari da 'yan tawayen Bakasi da ke yankin kudu masu yammacin Kamaru suka kai..

Sojoji a ƙauyen BakassiHoto: AP

Harin ta'addacin da ke zama irinsa na uku cikin mako guda da 'yan tawayen Bakasi na ƙasar kamaru suka kai ya haddasa mutawar mutane biyu. Jami'an sojen ƙasar suka ce wani sojan ƙundun bala ɗaya da kuma ɗan tawaye ɗaya ne dai suka rigamu guidan gaskiya a lokacin musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu. Hukumomin wannan ƙasa ba su bayyana sunan ƙungiyar da ta kai wannan hari ba. Sai dai shugaba Paul ya katse ziyarar aiki da ya ke yi a ƙasashen waje domin gudanar da wani taro na gaggawa da hafsoshin sojen ƙasar.

Manyan jami'an gwamnati da ke aiki a tsibirin har guda13 ne, 'yan tawayen ke garkuwa da su a halin yanzu da nufin samun diyya. Ana ci gaba da fiskantar tabarbarewan matakan tsaro a yankin mai arzikin man fetur da kuma kifi, wanda kotun ƙasa da ƙasa da mallaka wa Kamaru bayan shekaru tana taƙaddama akan tsibirin da makobciyarta wato Najeriya. 'Yan tawayen na neman hukumomi su gaggauta gudanar da ayyukan gina ƙasa a yankin. Yayin da wasun daga cikin ƙungiyoyin 'yan tawayen ke ci gaba da adawa da kasancewa ƙarƙarshin mulkin Kamaru.

Mawallafi: Mouhamadou Awal

Edita: Umaru Aliyu

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW