Najeriya: Taron APC ya tsayar da harkoki
March 27, 2026
Daukacin hanyoyin da suka nufi tsakiyar birnin Abuja zuwa dandalin da ake gudanar da wannan taron an rufe su kirif, inda motocin da ke da izini ne kadai ke da ikon ratsawa. Wannan ya tilasta an bai wa ma'aikatan gwamnati da ofisoshinsu ke a babbar sakatariya, umurnin su zauna gida. Matakin da gwamnatin Najeriyar ta dauka saboda babban taron na jam'iyyar APC mai mulki, ya shafi ma'aikata gwamnati har ma da na wasu kamfanonin 'yan kasuwa.
A bisa al'ada jam'iyyun siyasa a Najeriyar kan gudanar da manyan tarurrukansu a ranakun karshen mako ne, domin kaucewa kawo cikas ga aikin gwamnati da ma kai da komowar jama'a saboda kusancin dandalin da ake gudanar da taron da babbar sakatariyar ma'aikatan gwanati. Kwararu a fanin tsare-tsaren tattalin arziki a Najeriyar na bayyana cewa, lokaci ya yi da kasar za ta tsara yadda za a kaucewa kawo cikas ga ayyuka da harkokin kasuwanci a lokutan irin wadannan tarurruka da ma zabe.