SiyasaGabas ta Tsakiya
Isra'ila na gargadin 'yan Lebanon
December 15, 2023![Isra'ila | Kan Iyaka | Lebanon | Rikici | Hamas | Zirin Gaza | Falasdinu](https://static.dw.com/image/67147283_800.webp)
Talla
Takardun dai na gargadin fararen hular da kada su bayar da kariya ga mayakan kungiyar Hezbollah, suna mai bayyana su a matsayin gagarumar barazana da ka iya cutar da su. Jami'an tsaron Lebanon din dai sun bayyana cewa, an jefa takardun a wurare da dama da ke kan iyakar kasar da Isra'ila. Tun bayn da kungiyar Hamas da ke gwagwarmaya da makamai a yankin Zirin Gaza na Falasdinu ta kai harin ba-zata a Isra'ila a ranar bakwai ga watan Oktobar wannan shekara da muke ciki ne dai, ake samun musayar wuta tsakanin mayaka masu dauke da makamai kamar Hezbollah a bangaren kan iyakar Isra'ila da Lebanon din a hannu guda kuma da sojojin Isra'ilan a kan iyakokinsu.