Hukumomin Sudan sun jaddada matsayin su na watsi da dakarun Majalisar Ɗinkin Dunia a yankin Darfur
June 12, 2006Hukumomin ƙasar Sudan, sun jaddada matsayin su, na ƙin amincewa, da karɓar dakarun kwanta da tarzoma na Majalisar Ɗinkin Dunia, a yankin Darfur.
Mashawarcin ƙut da ƙut na shugaban ƙasa Omar El Beshir ya bayyana wannan sanarwa a yammacin jiya.
Majzub al- Khalifa Ahmed, ya mussanta batun maye gurbin dakarun kwantar da tarzoma na ƙungiyar Taraya Afrika, da na Majalisar Ɗinkin Dunia.
Ya ce yarjenejiyar da a ka rattaba hannu kanta, a birnin Abuja, tsakanin yan tawayen Darfur, da gwamnati ba ta ƙunshi matakin aika dakaru ba, daga Majalisar Ɗinkin Dunia.
A Ƙarshen shekara da mu ke ciki ne, komitin sulhu ke shirye shiryen, tura rundunar sojoji a yankin, bisa gayatar Ƙungiyar Taraya Afrika.
A cikin bayanin da ya yi kakakin shugaban El Beshir, ya bukaci kaɗai, Ƙungiyar AU, ta ƙarffafa dakararun ta a yankin.