1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ibrahim Gambari ya gana da hukumomin Burma

November 4, 2007

Wakilin mussaman na Majalisar Ɗinkin Dunia a ƙasar Burma kokuma Myanmar Ibrahim Gambari, ya sake komawa wannan ƙasa, a yunƙurin sa, na lalubo bakin zaren warware rikicin da ta ke fuskanta.

A safiyar yau, ya gana da ministan harakokin wajen Myanmar, da kuma ministan ƙwadago Aung Kyi, wanda gwamnatin mulkin sojan ƙasar ta naɗa, a matasyin mai tattanawa da shugabar yan adawa, Aung San Suu Kyi.

Ziyara ta Ibrahim Gambari, itace ta 2, tun bayan da ƙasar Myanmar ta tsinci kanta, cikin tashe-tashen hankulla a watan Satumba da ya wuce.

Saidai kuma ziyara na wakana, a lokacin da Gwamnatin mulkin soja ta yanke shawara kawo ƙarshen zaman shugaban tawagar Majalisar Ɗinkin Dunia, Charles Petrie a ƙasar.

Hukumomin Burma na zargin sa, da wuce gona da iri, da kuma shiga sharo ba shanu, a harakokin ta, na cikin gida.

Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Dunia ya bayyana takaici, a game da wannan mataki, ya kuma jaddada goyan bayansa, ga Charles Petrie, wanda ke jagorancin tawagar Majalisar Ɗinkin Dunia a Burma tun shekara ta 2003.