1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

ICC za ta yanke wa Ntaganda hukunci na karshe

March 30, 2021

Kotun hukunta masu aikata muggan laifuka ta  kasa da kasa , ICC, za ta yanke hukunci a wannan Talata a kan daukaka karar da jagoran wata kungiyar 'yan tawayen Kwango Bosco Ntaganda ya yi. 

Internationaler Strafgerichtshof Urteil Bosco Ntaganda
Hoto: Reuters/P. Dejong

Tun a shekarar ta 2019 ne dai kotun da ke birnin Hague ta same shi da laifukan da suka hada da kisa da cin zarafin mata da kananan yara  a lokacin da kungiyarsa ke tashen kaddamar da hare-hare a jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango. A bisa wannan kotun ta yanke masa hukuncin shekaru 30 a gidan maza. 

Sai dai Ntaganda wanda tsohon janar ne na soja da ya rikide ya koma dan tawaye ya musanta zarge-zargen, inda lauyoyinsa suka ce kotun ta ICC ta tabka kurarai a cikin hukuncin nata.

A shekarar 2013 dakarun gwamnatin Kwango suka murkushe kungiyar 'yan tawaye ta M23 da Ntaganda ya jagoranta kuma a wannan shekara shi da kansa Ntaganda ya yi saranda inda ya mika kansa ga ofishin jakadancin Amirka da ke birnin Kigali na Ruwanda.