1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ICC ta yi watsi da buƙatar sakin Gbagbo

October 27, 2012

Babbar kotun duniya da ke hukunta manyan laifukan yaƙi ta yi watsi da buƙatar da lauyoyin tsohon shugaban ƙasar Côte d'Ivoire suka gabatar na a yi masa sakin wucin gadi.

Former Ivory Coast President Laurent Gbagbo, center, and security guards are seen as Gbagbo appears for the first time at the International Criminal Court to face charges of crimes against humanity in The Hague, Netherlands, Monday, Dec. 5, 2011. Gbagbo was extradited to the Netherlands last week to face charges including murder and rape committed by supporters as he attempted to cling to power. (Foto:Peter Dejong, Pool/AP/dapd)
Hoto: dapd

Lauyoyin Gbagbo suka ce sakin wucin gadi zai ba wa tsohon shugaban Côte d'Ivoire samun ƙarin kuzari da lafiya wajen fuskantar shari'a da za a yi masa nan gaba. A lokacin da ya ke magana a wani zaman da kotun ta yi babban alƙali mai gabatar da ƙara ya sanar da cewar ba da belin Laurent Gbagbo mai yawan magoya baya na iya zama barazana ga ci gaba da gudanar da bincike a shari'ar da za a yi masa.

Tsohon shugaban mai shekaru 67 da haifuwa wanda ake tsare da shi a kotun ta duniya da ke a birnin Haye tun a cikin watan Mayon shekara ta 2011, ana tuhumar sa da aikata kisan gila akan farar hula a lokacin da aka gudanar da zaɓɓukan ƙasar a shekarun 2010 zuwa 2011.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Mohamadou Balarabe Awal