1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Idriss Deby da Omar El-Beshir ba su halarci ba taron Dakar

August 10, 2006

Shugaba Idriss na Tchad, da takwaran sa, Omar El Beshr na Sudan, sun ƙi amsa gayatar da shugaban ƙasar Senegal Abdullahi Wade, yayi masu a birnin Dakar, a yunƙurin sasanta rikicin da ke tsakanin su.

Jiya laraba ne a ka tsara cewar, shugabanin za su haɗu a Dakar, tare da mai masaukin baƙi, domin ɗinke barraka da ta kunno kai tsakanin su, bayan da Idriss Deby, ya zargi AL Bashir, da rura wutar rikicin Tawaye a Tchad.

Maƙwabtan 2 masu gaba da juna, sun haɗu iya, a birnin N´Dajmena albarkacin bikin rantsar da Idriss Deby.

A sakamakon ganawar da su ka yi, shugaba Ƙhaddafi na kasar Lybia, ya bayana samun nasara sasanta su.

Wani jami´in ƙasar Senegal,ya zargin Ƙhadafi, da yin ƙafar angullu, ga haduwar ta birnin Dakar, saboda hasada.

A cewar sa ,bayan kasawar da shugaban ƙasar Lybia yayi, na shawo kan wannan rikici, ba shi buƙatar ganin wani ya samu nasara.

Ya zuwa yanzu, babu wata sanarwa a hukunce, da ta hito daga fadar gwamnatocin ƙasashen domin bayyana dalilan da su ka hana wanzuwar wannan taro.