Iraki: Bam ya kashe mutane a bikin Aure
March 9, 2017![Irak Bagdad Bomben Anschlag](https://static.dw.com/image/37572352_800.webp)
Talla
Likitoci da ke karban jinya sun ce akwai mutane 25 da ke fama da munanan raunuka, sai dai kawo yanzu babu wadanda suka dau alhakin kai harin, amma hukomi a kasar sun ce kungiyar IS ta sha kai hare-hare makamancin wannan a kan fararen hula da ma jami'an tsaro.
A yanzu dai dakarun gwamnatin Iraki na fafatawa a yammacin birnin Mosul na ganin sun karbe iko na sauran yankunan da ke karkashin ikon kungiyar ta IS, inda wasu rahotanni ke cewa tuni jagoran kungiyar Abu Bakr al-Baghdadi ya tsere daga birnin.