Iran da Amurka sun fara ganawar kauce wa yaki
February 26, 2026
Talla
Tattaunawar da Oman ke shiga tsakani ta biyo bayan barazanar da Donald Trump ya yi ta yi na kai hari kan Iran, inda shugaban Amurka a ranar Alhamis da ta gabata ya bai wa Tehran kwanaki 15 don cimma yarjejeniya.
Tawagar Amurka da ta Iran sun isa wurin tattaunawar da ke gidan jakadan Oman a Geneva cikin tsauraran matakan tsaro, bayan zanga-zangar da 'yan gudun hijira na Iran suka yi lokacin tattaunawarsu a makon da ya gabata.
Ministan harkokin wajen Oman Badr Albusaidi ya tabbatar da cewa an fara tattaunawa, yana mai cewa bangarorin biyu sun bayyana budaddiyar fahimta ga sabbin dabaru da laluben mafita daga wannan rikici.
Gabanin tattaunawar da shugaban Iran ya dage cewa jamhuriyar Musulunci ko kadan ba ta kera ko neman makamin nukiliya.