Iran da Isra'ila na ci gaba da kai wa juna farmaki
March 7, 2026
Isra'ila ta ce ta kaddamar da sabbin jerin hare-hare ta sama a Tehran, babban birnin Iran. An yi ta wallafa hotunan da ke nuna yadda wuta ke tashi tare da turnukewar hayaki daga filin jirgin sama na Mehrabad bayan harin, filin jirgin da ke zama babbar tashar zirga-zirga ta cikin gida a Iran. An kuma bayar da rahoton cewa an jiyo tashin ababen fashewa a birnin Kudus da kuma wasu biranen yankin Gulf ciki har da Dubai da kuma Manama.
Karin bayani: Na rufe kofar tattaunawa da Iran - Trump
Ita ma rundunar sojin Iran ta ce, sojojinta sun kaddamar da hare-haren jirage marasa matuka kan Isra'ila da ma wasu sansanonin Amurka da ke kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da kuma Kuwait. A cikin sanarwar da kamfanin dillancin labaran Iran din ya fitar, ya ce an kai hare-haren ne kan sansanin sojin Al Minhad da ke Hadaddiyar Daular Larabawa, da kuma wani wuri da Iran din ta bayyana a matsayin mai matukar mahimmanci ga a Isra'ila.