1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran na kokarin sasanta Indiya da Pakistan

May 5, 2025

Kasar Iran ta kasance kasar farko da ke kokarin ganin an daidaita tsakanin Indiya da Pakistan, a sabon rikicin nan na diflomasiyya da ya sake kunno kai a tsakaninsu.

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar na karbar bakuncin takwaransa na Iran, Abbas Araghchi
Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar na karbar bakuncin takwaransa na Iran, Abbas AraghchiHoto: Ministry of Foreign Affairs of Pakistan/AFP

Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araghchi ya gana da manyan jami'an gwamnatin Pakistan a wannan Litinin, ganawar kuma da ke da nufin shiga tsakani domin warware rigimar da ta taso tsakanin Pakistan da Indiya.

Dagantaka dai ta kara yin tsami a tsakanin Pakistan din da Indiya ne, bayan wani kazamin hari da aka kai kan wasu Indiyawa 'yan yawon shakatawa a yankin Kashmir.

Ziyarar ta Abbas Araghchi a Islamabad ita ce ta farko da wani babban jami'i ke kaiwa da nufin duba rigimar da ta janyo asarar rayukan mutane 26 a ranar 22 ga watan jiya a garin Pahalgam na Kashimr.

Pakistan dai ta yi ta musanta laifin da Indiya ta dora mata na kasancewa da hannun a mutuwar bakin 'yan yawon shakatawa.