Sakamakon fadowar wani karfe wanda ya haifar da turmutsutsu
September 25, 2015![Iran Politik Eshagh Jahangiri](https://static.dw.com/image/16795219_800.webp)
Talla
Mahukuntan kasar Iran sun bukaci Saudi Arabiya data sanya kasashen su cikin wani kwamitin bin ba'asin abi nda ya faru sakamakon fadowar wani karfe wanda ya haifar da turmutsutsu a inda mahajjata sama da dari 700 suka rigamu gidan gaskiyya ciki hadda Iraniyawa 131 yayin aikin hajjin banan.
Mataimakin shugaban kasar Eshaq Jahangiri shi ne ya bayyana haka a yayin wani zaman majalisar zartarwar kasar a jumma'ar nan, a inda ya kara da cewar kasashe irinsu Iran na daya daga cikin kasashen da suka fuskanci mawuyacin hali sakamkon iftila'in don haka kamata yayi a sanya ta cikin kwamitin bin kadin abin da ya faru.