1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran na samun ci gaba a sarrafa sanadarin Uranium

April 11, 2006

Shugaba Mahmud Ahmadinajad na Iran, ya tabbatar da cewa an samu ci gaba dangane da sarrafa sanadarin Uranium da kasar sa keyi.

Bisa hakan, shugaban ya tabbatar da cewa a yanzu haka Iran na daga cikin sahun kasashen duniya dake da fasahar kera makamin nukiliya.

Shugaban daya fadi hakan a dazu dazun nan , a wani taron manema labarai daya gudanar, ya kara da cewa kasar zata ci gaba da sarrafa sanadarin na Uranium har zuwa lokacin da zata cimma burin data sa a gaba.

Shugaba Ahmadinajad, wanda yake ci gaba da fuskantar suka daga kasashen yamma a game da wannan aniya, ya kara nanata cewa nukiliyar da suke kokarin kerawa ta inganta rayuwar yabn kasar ce , amma bata tashin hankali ba.