Iran ta kalubalanci matakin Amurka game da baki
June 7, 2025
Talla
Hukumomin na Iran dai sun bayyana abin da Amurkar ta yi, da wani nau'i na nuna dabi'ar wariyar launin fata.
A ranar Larabar makon jiya ne dai Shugaba Donald Trump ya sanya hannu kan dokar hana kasashe 12 shiga Amurka, yana mai kafa hujja da dalilai na tsaro.
'Yan kasashen da Amurkar ta hana shiga cikinta baya ga Iran din dai, su ne Afghanistan da Myanmar da Chadi da , Congo-Brazzaville da Equatorial Guinea da Eritrea da kasar Haiti da Libya da Somalia da Sudan da ma kasarYemen.
Akwai ma wasu kasashen bakwai da aka kakaba musu tasu dokar wadda ba ta kai wadannan tsauri ba.