1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta sake kulle Mashigar Hormuz

April 18, 2026

Tun da fari Iran ta yi barazanar sake rufe Mashigar Hormuz idan Amurka ba ta cire takunkumin da ta sanya wa jiragenta a tekun Gabas ta Tsakiya ba.

Iran Qeschm 2026 | Tanker in der Straße von Hormus vor der Küste der Insel Qeschm
Hoto: Asghar Besharati/AP Photo/picture alliance

Gwamnain Tehran ta ce ta dauki matakin sake kulle Mashigar Hormuz ne yayin da Amurka ke ci gaba da toshe tashoshin ruwanta. Sanarwar hakan na zuwa ne bayan da Shugaba Trump ya ce ba za a sassauta takunkumin ga Iran ba, har sai Iran din ta amince da wasu shirye-shirye ciki har da shirinta na Nukiliya.

Karin bayani: Iran ta sanar da bude mashigar Hormuz

Sai dai duk da fargabar da ake da ita, jami'ai a Pakistan na cewa Amurka da Iran na kara matsawa ga cimma yarjejeniya kafin ranar 22 ga wannan watan na Afrilu, da ke zama wa'adin yarjejeniyar tsagaita wuta ta wucin gadi da aka cimma.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW