Iran ta shirya tsananin hukunci kan masu adawa da gwamnati
January 13, 2026
Talla
GWamnatin kasar Iran na tuhumar masu zanga-zangar da ta rikide tare da karade kasar ne da yin fito-na-fito ne da tsari na Ubangiji, laifin kuma da shari'ar Musulunci ke kaiwa ga yanke hukuncin kisa a kansa.
A ranar Litinin ne, babban alkalin kasar ya yi kira a kan hukunci ga masu zanga-zangar da suka kai hari kan ‘yan sanda da sauran wuraren tsaro.
A baya dai lokacin zanga-zangar da aka yi a 2022, akalla mutane 12 aka aiwatarwa da hukuncin kisa bayan zanga-zangar da ta shafi nema wa mata 'yanci.
Kungiyoyin kare hakkin dan Adam sun ce sama da mutane 640 sun mutu a zanga-zangar da ta fi girma tun 2022.
Wani jami'in Iran ya ce kimanin mutane 2,000 ne suka mutu tun farkon zanga-zangar makonni biyu da suka gabata.