SiyasaAfirka
Tehran ta harba tauraron dan adam
June 26, 2022![Iran | Zuljanah-Satellit](https://static.dw.com/image/62268246_800.webp)
Talla
Iran ta harba wani tauraron dan adam a wannan lahadi na gwajin fasahar sadarwa wato satellite, wannan shi ne karo na biyu da take harba tauraron mai suna Zuljanah wato bayan wanda tayi a bara.
Kasar na fatan ganin ta yi amfani da fasahar a fannoni sadarwa da suka hada da rediyo da talabijin da sauransu, baya ga iya amfani da shi a wasu gwaje-gwajen fasahohi na zamani. Mahukuntan na Tehran ba su fito sun yi karin bayani kan nasarar gwajin tauraron ko kuma akasin hakan ba kamar yadda ta saba fadi a baya.