1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Tehran ta harba tauraron dan adam

Ramatu Garba Baba
June 26, 2022

Karo na biyu kenan da kasar Iran ke harba tauraron dan adam zuwa sararin samaniya a binciken da Tehran ke yi kan gwajin fasahar sadarwa.

Iran |  Zuljanah-Satellit
Hoto: Farsnews

Iran ta harba wani tauraron dan adam a wannan lahadi na gwajin fasahar sadarwa wato satellite, wannan shi ne karo na biyu da take harba tauraron mai suna Zuljanah wato bayan wanda tayi a bara. 

Kasar na fatan ganin ta yi amfani da fasahar a fannoni sadarwa da suka hada da rediyo da talabijin da sauransu, baya ga iya amfani da shi a wasu gwaje-gwajen fasahohi na zamani. Mahukuntan na Tehran ba su fito sun yi karin bayani kan nasarar gwajin tauraron ko kuma akasin hakan ba kamar yadda ta saba fadi a baya.