Iran za ta kai hari sansanonin Amurka na Gabas ta Tsakiya
February 7, 2026
Iran ta sha alwashin kai hari kan sansanonin Amurka da ke Gabas ta Tsakiya, matukar ta kuskura ta kai ma ta hari, kuma kada kasashen yankin su dauki cewa su ta kai wa hari, face Amurka.
A tattaunawarsa gidan talabijin na Al Jazeera ranar Asabar, kwana guda bayan kammala tattaunawar zangon farko tsakanin Tehran da Washington, a birnin Musqat na kasar Oman, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, ya shaida cewa kofarsu a bude take, don ci gaba da tattaunawar, ko da ya ke ba a kai ga tsayar da rana ba.
Karin bayani : Shugaba Trump ya ce Iran ta kagu ta cimma sulhu da Amurka
Tuni aka jiyo shugaba Donald Trump na Amurka na cewa a farkon mako mai kama ne za su ci gaba da tattaunawa da Iran, kan batun kwance damararta ta kera makamin nukiliya da ma sauran batutuwan tsaro.