1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta kai sabbin hare hare a Beirut

Abdullahi Tanko Bala
November 1, 2024

Israila ta yi luguden wuta a yankin Dahiye da ke kudancin birnin Beirut inda ta lalata gidaje da dama sai dai babu dai rahoton hasarar rayuka.

Harin Isra'ila a yankin Dahiyeh na Beirut
Hoto: Hassan Ammar/AP Photo/picture alliance

A baya bayan nan Israila ta tsananta hare hare ta sama a arewa maso gabas da kuma kudancin Lebanon. Masu shiga tsakani na kokari domin samun yarjejeniyar tsagaita wuta a Lebanon da kuma Gaza.

Ma'aikatar lafiya ta Lebanon ta ce mutane fiye da 2,800 suka rasa rayukansu yayin da wasu 13,000 kuma suka sami raunuka tun daga ranar 8 ga watan Oktoba lokacin da Hizbullah ta fara harba rokoki zuwa cikin Israila.

Yawan mutanen da suka rasu a yakin Israila da Hamas a Gaza ya haura mutum 43,000 yayín da harin da Hamas ta kai wa Israila na ranar 7 ga wata Oktoba ya hallaka 'yan Israila 1,200 yawancin su fararen hula ta kuma yi garkuwa da wasu mutanen 250

 

 

 

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW