Isra'ila ta kai sabbin hare-hare a Lebanon
March 8, 2026
Talla
Yayin da aka shiga mako na biyu na rikicin yakin Gabas ta Tsakiya, ma'aikatar lafiya ta kasar ta ce a kalla mutane takwas ne suka jikkata a harin da aka kai kan wani otel a birnin Beirut na Lebanon a safiyar wannan Lahadin. Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kai harin ne kan kwamandojin dakarun na juyin-juya-halin Iran wato IRGC da ke Beirut din.
Karin bayani: Fafutukar sasanta rikicin Yankin Gabas ta Tsakiya
Rahotanni sun yi nuni da cewa, hare-haren na wannan safiyar sun shafi wata cibiyar mai da ke Tehran da ma wasu wurare a Iran. Sabbin farmakin na zuwa ne bayan da shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian ya nemi afuwar kasashe makwaftan Iran kan hare-harenta.