Isra'ila ta kai wasu sabbin hare-hare a Gaza
January 31, 2026
Talla
Sabbin hare-haren na zuwa ne kwana guda bayan da Isra'ila ta zargi Hamas da saba ka'idojin tsagaita bude wuta.
Har ila yau jerin hare-haren sun zo ne gabanin cika ranar da Isra'ila ta yi alkawarin bude mashigar Rafah da ke kan iyaka da Masar, wani muhimmin mataki a yarjejeniyar da aka cimma a bara a matsayin hanyar kawo karshen yakin.
Ma'aikatar lafiya ta Gaza ta bayyana cewar sama da Falasdinawa 500 ne hare-haren Isra'ila suka hallaka tun bayan fara aiki da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a ranar 10 ga watan Oktoba shekarar 2025.
Karin Bayani: Isra'ila ta binne gawar karshe da aka dawar daga Gaza