1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Isra'ila ta kashe mataimakin shugaban kungiyar Hamas

Mouhamadou Awal Balarabe
January 2, 2024

Saleh al-Arouri,da Isra'ila ta zarga da jagorantar hare-hare da dama, an zabe shi ne a matsayin mataimakin shugaban Hamas a 2017..Wannan dai shi ne karon farko tun bayan fara yakin Gaza da Isra'ila ta kai hari a Beirut.

Mataimakin shugaban Hamas Saleh al-Arouri
Mataimakin shugaban Hamas Saleh al-ArouriHoto: IRNA

Mataimakin shugaban kungiyar Hamas Saleh al-Arouri ya gamu da ajalinsa, a wani harin da Isra'ila ta kai a kusa da birnin Beirut na kasar Lebanon. Wannan dai shi ne karon farko tun bayan fara yakin Gaza, da Isra'ila ta kai hari a babban birnin kasar Labanon. A baya dai, fadan da ake gwabzawa tsakanin sojojin Isra'ila da kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon da ke kawance da Hamas na takaita ne a  kan iyaka da ke kudancin kasar.

Karin bayanZirin Gaza: Mutane na ci gaba da halakai: 

Hamas ta tabbatar da wannan kisan, yayin da kamfanin dillancin labaran kasar Lebanon (ANI) ya ce wasu karin mutane hudu sun mutu a harin da Isra'ila ta kai. Shi dai Saleh al-Arouri, wanda Isra'ila ta zarga da jagorantar hare-hare da dama, an zabe shi ne a matsayin mataimakin shugaban Hamas a 2017. Dama dai ya fita daga gidan yari ne a 2010 bayan da ya shafe kusan shekaru 20 a gidan yarin Isra'ila​.

Karin bayani: Gaza: Masar da Qatar na neman a tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta

Ita kuwa kungiyar Hamas ta ce a shirya take ta ba da hadin kai wajen kafa gwamnatin Falasdinawa daya tilo a yankin yammacin kogin Jordan da kuma zirin Gaza. Shugaban wannan kungiya Isma'il Haniyeh da kansa ne ya yi wannan bayyani a wani jawabi da aka watsa ta kafar talabijin, inda ya ce sun samu shawarwari da dama game da wannan mataki sakamakon yakin da ake fama da shi a Zirin Gaza.

Karin bayaniShirin wata sabuwar yarjejeniya tsakanin Isra'ila da Hamas:    

Sai dai Haniyeh ya bayyana cewar ba za a sako 'yan Isra'ila da suka yi garkuwa da su a Gaza ba, matikar ba a amince da sharadi da Hamas za ta gindaya ba. Idan za a iya tunawa dai, kungiyar Hamas tana ci gaba da yin garkuwa da mutane 129 daga cikin 250 da ta kama bayan da ta kai wa Isra'ila mummunan hari a ranar 7 ga watan Oktoban bara.