SiyasaGabas ta Tsakiya
Isra'ila ta kashe sama da mutane 300 a Lebanon
April 9, 2026
Talla
A cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta kara da cewa jimillar adadin wadanda suka mutu tun farkon rikicin tsakanin Isra’ila da ƙungiyar Hezbollah mai goyon bayan Iran a ranar 2 ga Maris ta kai 1,888 da jikkata mutane dubu 6 da 92.
Ma’aikatar ta yi gargadi cewa adadin mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa yayin da ake ci gaba da ayyukan bincike da gwajin DNA na gawawwakin da aka kai asibitoci. Gamayyar kasashe sama da 60 da suka girka dakarun kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya sun yi Allah wadai da kashe jami'ai uku a yakin Lebanon.
Kasashen da suka hada da Indonesiya, da Faransa, da birtaniya, da China da Turkey da kuma Rasha, sun yi kira ga Isra'ila da Hezbollah su dakatar da rikicin.