1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta sake aika dakaru zuwa Siriya

May 4, 2025

Rundunar sojin Isra'ila, ta ce ta aike da dakarunta zuwa kudancin Syria, duk kuwa da Alla-Wadai din da Majalisar Dinkin Duniya ta yi da abin da kasar ke yi a Syriar a 'yan tsakanin nan.

Wasu mayakan Isra'ila a iyakar Siriya
Wasu mayakan Isra'ila a iyakar Siriya Hoto: Mati Milstein/NurPhoto/picture alliance

Wannan wani shiri ne nata a cewar rundunar, da ke nufin dakatar da sojojin Siriya daga shiga kudancin da ke dauke da matsugunan 'yan kabilar Druze marasa rinjaye.

Sojojin na Isra'ila dai ba su bayar da adadin mayakan da aka aike da su zuwa kudancin na Siriya ba.

Gwmanatin Firaminista Benjamin Netanyahu dai ta tsaurara sintirin soji a kudancin Syria ne, tun bayan kawo karshen gwamnatin Bashar al-Assad a cikin watan Disamba.

Ko a ranar Juma'a ma dai Isara'ilar ta kaddamar da wasu hare-are ta sama a kusa da fadar shugaban kasar Siriya da ke a Damascus babban birnin kasar.

Hare-haren dai na zuwa ne bayan kalaman da Netanyahu ya yi na cewar Isra'ila za ta tsoma hannunta, muddin dai gwamnatin Siriya ta yanzu ta ki kare tsirarun 'yan kabilar Druze.