Isra'ila ta saki kuɗaɗen harajin Falasɗinu
March 25, 2013![Israeli Prime Minister Benjamin Netanyahu chairs the Likud-Beiteinu faction meeting at the Knesset (Israel's Parliament) on March 14, 2013 in Jerusalem. Netanyahu is to formally unveil the shape of his long-awaited coalition government which will be sworn in just days before a visit by US President Barack Obama. AFP PHOTO/GALI TIBBON (Photo credit should read GALI TIBBON/AFP/Getty Images)](https://static.dw.com/image/16678141_800.webp)
Talla
A cikin wata sanarwa da ofishin fira ministan ta sanar, ta ce an yanke shawarar ne a ƙarshen wani taron majalisar ministocin. A cikin watan Disamba na shekarar bara ne, Isra'ila ta dakatar da shirin, bayan da Majalisar Ɗinkin Duniya ta amince da Falasɗinu a matsayin yar kallo a majalisar.
Sannan ta ummarci ministan kuɗi na ƙasar da ya zuba kuɗaɗen ga hukumar Falasɗinawan. Hakan kuwa na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurika Barack Obama ya kammala wata ziyara a yankin gabas ta tsakiya. Masu yin sharhi a kan al'amura na ganin wannan mataki zai taimaka a samu ƙarin fahimtar juna tsakanin ƙasashen biyu.
Mawallafi : Abdourahamene Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh