1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta tsananta kai hare-hare a Iran

June 15, 2025

Isra'ila ta ci gaba da hare-harenta zuwa Iran tare da barazanar da amfani sosai bayan wasu makaman Iran sun fada cikin kasar. Rayuka dai na salwanta a kwanaki uku da fara kai wa juna hare-hare.

Hare-haren Isra'ila a cikin kasar Iran
Hare-haren Isra'ila a cikin kasar IranHoto: Ahmad Hatefi/UPI Photo/IMAGO

Isra'ila ta ci gaba da kai hare-harenta ta sama a fadin Iran tare da barazanar yin amfani ka karfi fiye da kima, bayan wasu makaman Iran sun tsallaka zuwaa Isra'ila inda suka fada a kan gine-gine a tsakiyar kasar.

An dai kai ga soke tattaunawar da aka shirya yi a yau Lahadi a kan shirin nukiliyar Iran, wanda zai iya zama hanyar samun sulhu.

Hare-haren Isra'ila cikin kwanaki uku, sun yi sanadiyar mutuwar akalla mutane 406 a Iran tare da raunata wasu 654, a cewar wata kungiya mai rajin kare hakkin dan Adam da ke Washington, wadda ta dade tana bibiyar al'amuran kasar.

A takaice, rikicin ya shiga wani sabon mataki na tashin hankali mai tsanani, inda hare-hare ke kara ta'azzara tsakanin Isra'ila da Iran, yayin da kasashen duniya ke kira ga zaman lafiya da tattaunawa.