Isra'ila ta tsananta kai hare-hare a Iran
June 15, 2025
Isra'ila ta ci gaba da kai hare-harenta ta sama a fadin Iran tare da barazanar yin amfani ka karfi fiye da kima, bayan wasu makaman Iran sun tsallaka zuwaa Isra'ila inda suka fada a kan gine-gine a tsakiyar kasar.
An dai kai ga soke tattaunawar da aka shirya yi a yau Lahadi a kan shirin nukiliyar Iran, wanda zai iya zama hanyar samun sulhu.
Hare-haren Isra'ila cikin kwanaki uku, sun yi sanadiyar mutuwar akalla mutane 406 a Iran tare da raunata wasu 654, a cewar wata kungiya mai rajin kare hakkin dan Adam da ke Washington, wadda ta dade tana bibiyar al'amuran kasar.
A takaice, rikicin ya shiga wani sabon mataki na tashin hankali mai tsanani, inda hare-hare ke kara ta'azzara tsakanin Isra'ila da Iran, yayin da kasashen duniya ke kira ga zaman lafiya da tattaunawa.