1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

ISWAP ta dauki alhakin halaka kiristoci a Arewacin Najeriya

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
April 22, 2025

Daga cikin harin har da wanda suka kai barikin sojojin garin Yamtage da suka kona a jihar Borno, bayan halaka sojoji uku

Sojojin Najeriya
Hoto: AFP/Getty Images

Kungiyar ta'addanci ta ISWAP ta yi ikirarin daukar alhakin munanan hare-haren da aka kai kan sansanonin jami'an tsaro, da kuma fararen hula kiristoci a yankin Arewacin Najeriya, a farkon watan Afirilun 2025.

Wannan na cikin sakonni bakwai da kungiyar ta wallafa a kafar yada labaranta ta Amaq, ciki har da fayafayan bidiyo biyu da kundin hotunan da ke zayyana yadda suka kitsa hare-haren ta'addancin.

Karin bayani:ISWAP ta kashe jami'an tsaron Najeriya

Daga cikin hare-haren har da wanda suka kai kan barikin sojoji na garin Yamtage da suka kona a jihar Borno, bayan halaka sojoji uku, sannan suka kama jami'an sa-kai hudu da ke aiki da sojojin suka kashe a jihar.

Karin bayani:Nakiya ta hallaka mutum 10 a Najeriya

Haka zalika a jihar Adamawa sun kai hare-hare biyu a kauyukan Lareh da Banga, da mafi akasarin al'ummarsu kirsitoci ne, suka kashe mutane biyu suka kona gidaje 30 da kuma majami'a daya, kamar yadda suka wallafa hotunan a jaridarsu, har ma da lalata motar 'yan sanda bayan jikkata su.