1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagoran RSF ya gana da 'yan siyasar Sudan

January 2, 2024

Ganawar da suka yi a ranar Litinin na zuwa ne bayan da masu hankoron kare dimukuradiyya a Sudan suka zargi rundunar ta RSF da halaka fararen hula tare da kwashe musu dukiya da sunan ganima a wasu yankuna na Sudan.

Hoto: Mahmoud Hjaj/AA/picture alliance

Jagoran mayakan rundunarRSF a Sudan Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya yi wata ganawar sirri da 'yan siyasar kasar a birnin Addis Ababa na Habasha, daidai lokacin da mayakansa ke ci gaba da ikirarin samun galaba a yakin da kasar take ciki na watanni tara.

Karin bayani: Sarkakiya da ke tattare da rikicin Sudan

A hannu guda kuma shugabannin kasashen Yuganda da Habasha da Djibouti duk sun gana da Janar Dagalo wanda ake wa lakabi da Hemedti kuma ke ayyana kansa a matsayin shugaban Sudan wacce rikici ya daidaita mutanenta. Sai dai jagoran sojin Sudan Abdel Fattah al-Burhan  ya bayyana ganawar da wadannan kasashe suka yi da Janar Dagalo a matsayin abin da bai dace ba.