1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Jagorar adawar Faransa Le Pen na fuskantar tuhuma a kotu

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
September 30, 2024

Daga cikin mutane 28 da ke fuskantar tuhumar har da mahaifinta Jean-marie Le Pen, wanda ya kafa jam'iyyar RN mai tsattsauran ra'ayi a Faransa.

Hoto: Maillard/Maxppp/Imago

A Litinin ce 30.09.2024, jagorar 'yan adawar kasar Faransa Marine Le Pen za ta fara gurfana a gaban kotu tare da wasu mukarrabanta, don fuskantar tuhuma kan almundahar kudi da almubazzranci da dukiyar kasa. Daga cikin sauran mutane 28 da ke fuskantar tuhumar, har da mahaifinta Jean-marie Le Pen, wanda shi ne ya kafa babbar jam'iyyar adawar ta National Rally.

Karin bayani:Faransa: Bardella ya maye gurbin Le Pen

Zarge-zargen na da alaka da badakalar da ta wakana daga shekarar 2004 zuwa 2016, inda ake zargin Marine da mahaifinta da karbar Euro miliyan 7 daga hannun majalisar dokokin tarayyar Turai, amma suka karkatar da akalar kudin zuwa ga gina jam'iyyarsu. Da zarar an same su da laifin, za su fuskanci hukuncin daurin shekaru 10 a kurkuku da tara, da kuma haramta musu shiga siyasa har na tsawon shekaru biyar.