Jagorar 'yan adawar Taiwan ta gana da shugaba Xi Jinping na
April 10, 2026
A ganawar shugabannin a birnin Beijing, bangarorin biyu sun ce barakar da ake samu da ke haddasa rarrabuwar a tsakanin China da Taiwan na kan hanyar dinkewa. Tuni ziyarar ta janyo cece-kuce a fadin Taiwan inda masu adawa da manufofin Cheng Li-wun ke ganinta da nuna zakewa kan manufifin Bejin fiye da kima.
Karin bayani:Taiwan na bukatar zaman lafiya da China
Tun a shekarar 2016 ne dai gwamnatin Chinar ta dakatar da duk wata hulda da manyan masu fada ji a siyasar Taiwan bayan da jam'iyyar Democrat ta yankin ta yi fatali da kasancewar Taiwan a karkashin ikon wani bangare na kasar Sin, inda ta kara karkata alakarta da Amurka, lamarin da ya kai kasar ga gudanar da gagarumin atisayin soji a tekun yankin, a wani mataki na tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro.