1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Jagororin da ke rikici da juna a Sudan sun amince da ganawa

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
December 11, 2023

Rikicin Sudan din ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan dubu goma, a dalilin gwagwagwar kwatar ikon mulkin kasar tsakanin wadannan manyan Janar guda biyu, da a baya suka hada kai suka hambarar da Omar al-Bashir

Hoto: AFP

Jagororin bangarori biyu da ke rikici da juna a Sudan sun amince da ganawar keke-da-keke domin tattauna hanyoyin bi na tsagaita wuta, tare da kawo karshen zubar da jinin da aka shafe tsawon watanni ana yi a kasar, kamar yadda kungiyar raya kasashen Gabashi da kuma na Kahon Afirka IGAD ta sanar.

Karin bayani:Hari kan dam na barazanar haddasa ambaliyar ruwa a Sudan

Sanarwar ta fito ne bayan kammala taro a karshen mako a kasar Djibouti, da ya samu halartar Janar Abdel-Fattah al-Burhan da ke jagorantar Sudan, yayin da mai adawa da shi kuma jagoran dakarun RSF Janar Mohammed Hamdan Dagalo da aka fi sani da Hemedti da ba san inda yake ba aka tattauna da shi ta wayar tarho a taron.

Karin bayani:Dubban yara da suka tsere daga Sudan zuwa Chadi na fama da yunwa

Rikicin Sudan din ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan dubu goma, a dalilin gwagwagwar kwatar ikon mulkin kasar tsakanin wadannan manyan Janar guda biyu da ke ikirarin shugabancin kasar, wadda ta fada cikin rikicin shugabanci tun bayan da su biyun suka hada kai wajen hambarar da gwamnatin Omar al-Bashir.