Jami'an Amirka sun sauka Turkiyya
October 17, 2019![Mike Pence und Mike Pompeo](https://static.dw.com/image/50863730_800.webp)
Mataimakin shugaban kasar Amirka Mike Pence da sakataren harkokin wajen kasar Mike Pompeo, sun isa Ankara babban birnin kasar Turkiyyar, domin tattaunawa kan batun neman tsagaita buda wuta a yankin arewa maso gabashin Siriya.
Manyan jami'an biyu dai za su gana ne da Shugaba Racep Tayyip Erdogan a kan batun da shugaban na Turkiyya ya yi ta yin biris a kai.
Hasali ma bayyana rashin damuwarsa Mr Erdogan din ya yi da barazanar kakaba wa kasarsa takunkuman tattalin arziki da musamman kasar Amirka ta yi.
Mike Pence, wanda ke shiga Turkiyya a karon farko a matsayinsa na mataimakin shugaban Amirka, ya sauka Turkiyyar ne 'yan sa'o'i bayan nesanta kansa da Shugaba Donald Trump daga rikicin Turkiyya da Kurdawan arewacin na Siriya.
A kalaman nasa dai, Shugaba Trump, ya ce babu ta yadda hakan ya shafi Amirka.