1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jami'an tsaro sun kama mutane 900 a Senegal

Salissou BoukariJanuary 25, 2016

Hukumar 'yan sandan Senegal ta sanar a wannan Litinin din cewa, ta kama mutane a kalla 900 a wani bincike da ta aiwatar a tsarinta na yaki da ta'addanci a kasar.

Proteste gegen die Regierung in Dakar Senegal
Hoto: Reuters

Wannan bincike dai ya gudana ne a karshen makon da ya gabata sakamakon yawaitar hare-hare da ake samu a yankin Yammacin Afirka inda a ranar 20 ga watan nuwamba wasu 'yan ta'adda suka kai hari a wani babban Hotel na birnin Bamako, sannan a ranar 15 ga wannan wata na Janairu a wani babban Hotel na birnin Ouagadougou abun da ya kai hukumomin na Senegal ga daukan wannan mataki na riga kafi.

A ranar 21 ga wannan watan ne dai ministan cikin gidan kasar ta Senagal ya sanar a gaban 'yan majalisun dokokin kasar cewa ya baiwa jami'an tsaron kasar izinin aiwatar da wannan bincike.

 

 

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW