1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam´iyun adawa a ƙasar Guine-Conakry sun buƙaci a girka gwamnatin riƙwan ƙwarya

March 21, 2006

Jam´iyun adawa a ƙasar Guine Konakry, sun buƙaci a girka gwamnatin rikwan kwarya a dalilin da rashin lahiyar da shugaban ƙasar Lansana Konte, ke fama da ita.

A yanzu haka, shugaban na kwance a wata asibitin ƙurraru da ke ƙasar Suizland.

Lansana Konte, ya daɗe, ya na fama matsanciyar cutar ciwon sukari.

Masu kulla da harakokin siyasa a wannan ƙasa, sun fara hasashen sojoji, su yi anfani da wannan dama, domin aiwatar da juyin mulki.

A cikin sanarwar da su ka hiddo a yau, yan adawar Guine-Konacry, sun yi dogaro da sakamakon tantanawar da aki yi, tsakanin jami´yun adawa, da ƙungiyoyin fara hulla, wanda shima, ya bayyana wannan buƙata.

Sun bada shawara girka gwamnatin riƙwan ƙwarya, ta tsawan watani 18, wace za a ɗorawa yaunin shirya zaɓe, da kuma wata hukuma, da za ta ƙunshi wakilan jam´iyun ƙasar baki ɗaya, da ƙungiyoyin fara hulla, wadda za ta maye gurbin majalisar dokoki.

Saidai wata sanarwa da opishin jikadancin Guine, a ƙasar Suizland ta hiddo a sahiyar yau ta bayyana cewar shugaba Lansana Konte ya fara samun sauƙi.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW